02/07/2025
Muna son aure kuma muna bukatarsa a yanzu haka, kowace yarinya harma da samari gamunan mun rasa inda zamu tsoma ranmu kullum sha'awa na yi mana barazana.
A duk lokacin da muka tuna cewa sabon Allah babu kyau sai mu shiga furgice, gashi yanzu abin dake motsa sha'awa babu wahala ko a social media ko a zahiri, me yasa iyaye basa yi mana adalci, magna ta domin Allah kasar Hausa muna cikin tashin hankali idan an kalli makomar mutuncinmu da tarbiyyarmu, maza bin mata kamar kuda da nama, mata bamu da aiki sai bayyana tsiraici a yanzu har munfi boye fuskarmu akan kirjinmu da mazaunai.
Shin sai yaushe ne iyaye da malamai da gwabnati zasu gane tashin hankali da barazanar da muke ciki a yau, dan Allah kuji tsoran Allah hakkinmu yana kanku, iyayenmu, malamanmu, shagabanninmu, yayunmu ku tausaya mana ita fa sha'awa halitta ce da ita muke kwana muke tashi duk yadda ka kai ga taka tsantsan wataran baka iya sarrafa kanka.
Mata muna son aure matsalarmu buri da rainuwa, amma wallahi yanzu da yawa munfi son aure ta kowanne hali, maza kuma basu da hali ga rayuwa tayi tsada, dan Allah a sauke farashin aure a rage wasu abubuwan da ba dole ba ne a addini ko zamu samu mu tsira da mutuncinmu.
Iyaye basa tunawa ko tunanin halin da yarinya ko yaro zai iya shiga basu damu su sauke nauyi ba amma da an samu matsala yarinya ta fara bin maza sai a shiga zarginta ana tsangwamarta bayan kuma anki mata aure.
Dan Allah duk wanda ya karanta yayi shere ko Allah zai sa a ankara.
Wallahi iya social media idan aka duba yadda ake raye-raye da bayyana tsiraici ansan muna bukatar mahadi, haka wane hira kullum dai ba magana.
Shere please