09/04/2026
QALBU (Zuciya) itace muhallin zaman Allah ko karɓar Tajallin Allah, amma ba kowace zuciya ba, sai zuciyar Arifi masani Allah. Shehu Aliyu Muhammad Bunza (QS) yace Zuciyar Arifi ita ce Haqiqanin بيت المعمور (BAITUL MA'AMUR), wanda a zahiri ance Shine bagiren da ke cikin sammai wanda da ke saiti da ɗakin ka'aba, Amma a haqiqa Ana Ishara ne da Zuciya mai Tsarki, ko dama ance ka'aba itace ɗakin Allah, Mun San cewa a zahiri ba Haka abin yake ba, Don Bazaka shiga ciki ka tarar da ALLAH ba (ya girmama ya ɗaukaka da Wannan), Wannan Ishara ne saboda dukkan tajalliyatu na Zahiri suna Ishara ne da wata haqiqa ta baɗini a cikin Allah, Ka'aba tana ishara da Zuciya, da aka ce dakin Allah ce ana nufin zuciya itace ɗakin Allah ko shi ba daki Kamar yadda muka sani ba inda Ake shiga a zauna, Idan aka ce dakin Allah ana nufin Muhalli na Zuhurin tajallin shi na baɗini, tajallin shi kuma ba tajalli guda bane da Zai sauka sauka guda shike nan, a'a, tajallin shi sassaukowa yake yi kowane Sakan daga Halarar Ruhi.
Shehu Aliyu QS yace abinda yasa Zuciya ta zama Baitul ma'amur shi ne, shi Baitul ma'amur ance bagire ne inda dubban Mala'iku ke ibada (Mala'iku 70,000) a kowace rana Kuma kuma ko wace rana Mala'ikun da zasu shiga daban suke da waɗanda s**a yi ibada Ranar da ta wuce, kuma Idan s**a tafi ba'za su sake dawowa ba har ranar qiyama. Shehu yace haka Zuciyar Arifi take, A Raye take da'iman kuma Wa'ridat da Anwar da asarar suna sauka a cikin ta kowane lokaci, Wa'ridin da ya sauka yanzu daban yake da wanda zai sauka ɗazu da wanda Zai sauka anjima, Wa'ridaun da zasu sauka Yau daban suke da waɗanda zasu sauka gobe, kayi tunani ka gani, tun zamanin Annabi Adam (As) har zuwa zamanin Annabi Muhammad SAW, zuwa zamanin waliyyan Halarar Muhammaadiyya zuwa zamanin Shehu Ahmad tijjani zuwa zamanin Faila har zuwa zamanin Sirrin Faila da muke ciki yanzu Wa'ridat Basu yanke ma zukatan Arifai manema Allah ba, kuma ko wane zamani, ko wace halara da kalar nasu Wa'ridin, ko cikin zamanin da Halarorin ko wane Sa'liki mai suluki da kalar nashi Wa'ridin, sannan dukkan su Haqa'iqu ne daga tushe guda wanda shine HALARAR ALLAH MAI TSARKI.
Shi yasa Zuciya ta zama Baitul ma'amur Don ko da yaushe a raye take tana karbar saƙwanni daga Halarar Allah, A luganance kalmar ma'amur tana da Alaƙa da Rayuwar mai tsayi wadda ba'a San ƙarshen ta ba.
Hisabin Qalbu Ɗari da Talatin da Biyu ne (132)
132 tajallin 66 sau Biyu (66*2), 66 shine Hisabin sunan الله.
132 sau biyu zai iya daukar tajallin ALLAH (66) Biyu zahiri da baɗini, ciki da waje, ko Qalbu ana qallaba ta cikin RUH da kuma NAFS da Aqlu, sannan Karɓar tajalli take yi anan aka samu Qabbala (karɓa).
Alhamdu lillah, Allah ya raya Muna zukatan mu da hasken shi da Asraran shi Zahiran wa baɗinan. Albarkacin MAWLANA QALBUL A'LAMEENA.
Daga shafin: Murtadha aliyu