Jibwis RIBAN GARMU

Jibwis RIBAN GARMU Missionaries

RAYUWA BAYAN RAMADAN !!!  Haƙiƙa ALLAH (ﷻ) Shi ne Ubangijin watannin nan goma sha biyu kuma wajibi ne musulmi ya bauta m...
02/04/2025

RAYUWA BAYAN RAMADAN !!!
Haƙiƙa ALLAH (ﷻ) Shi ne Ubangijin watannin nan goma sha biyu kuma wajibi ne musulmi ya bauta masa a bisa yadda ya buƙata, kuma ya nisanci saɓa masa a kowane haninsa, sawa'un a Ramadan ko a bayan Ramadan.
Bayin ALLAH su kanyi matuƙar ƙoƙari a lokutan da aka fifita su fiye da sauran wasu lokuta domin samun garaɓasa da Rahamar ALLAH (ﷻ), sai dai kash da yawa daga cikin Al'ummah s**an keɓance waɗannan lokutan ne kawai domin biyan buƙatun su, bayan waɗannan ƙayyadaddun lokuta sai su koma ga ayyukansu na saɓon ALLAH wa'iyazubillah. Ba haka ALLAH yake buƙata ba, ba haka musulmin ƙwarai yake kasancewa ba.
Imam Bishru Al-Haafiy (Rahimahullah) Ya ce: “Tir da mutanan da basa sanin haƙƙin ALLAH (ﷻ) sai a cikin watan Ramadan, lallai mutumin kirki shi ne Wanda yake bauta yake kuma ƙoƙari a dukkanin shekara.” [Laɗa'iful Ma'arif P:222]
Kada ka zama cikin mutanen da suke Farin ciki da rabuwa da Watan Ramadan, domin su cigaba da bin Sha’awarsu da yin saɓo, waɗanda aka kangesu daga gare su tsawon watan Ramadan da aka gabatar.
Imam Ibnul Jauzy (Rahimahullah) Ya ce: “Ya Kai wanda ya cika Ramadan da Mafi kyawawan ɗabi'u, kada ka canja bayan tafiyar sa.” [Attabswirah:]
Kayi ƙoƙari ka zama daga cikin mutanen da s**a kasance suna farin ciki da murnar ƙarewar Ramadan ne bayan cikar ayyukan su da fatan ALLAH Ya karɓi ibadun da s**a gabatar, sannan suke cigaba da ɗorewa da bin bayan shi da Istighfari da nafiloli na salloli da azumi.
Magabata sun kasance suna ƙara ƙoƙari a bayan Ramadan tare da tsoro da zulumi da damuwa ??? Tsoro akan me ???
Malik Bin Dinaar (Rahimahullah) Ya ce: “Tsoro akan tunanin an karɓa aikin ko ba a karɓa ba, shi yafi tsanani akan yin aikin.” [Laɗa'iful Ma'arif: 209]
Ibnul Fadl (Rahimahullah) Ya ce: “Su (magabata) suna shafe wata shida suna roƙon ALLAH Ya kai su Ramadan. Kuma suna shafe wata shida suna roƙon ALLAH Ya karɓa masu (ayyukan da su ka yi) a Ramadan.” [Laɗa'iful Ma'arif na Ibnu Rajab]
ALLAH Ya karɓa mana ibadun mu da muka gabatar a Ramadan Ya kuma ƙarfafe mu da cigaba da ayyukan alkhairi ya nisanta mu daga Shaiɗan da Shaiɗanun mutane, kuma ya maimaita mana Ramadan da alkhairi (Aameen)

BAYYANAR MUMMUNAR AƘIDAR SHI'A A RIBAN GARMU DA SAURAN GARURUWANMU (1)Lallai yazama dole muyi bayanin A kan illar wannan...
03/11/2024

BAYYANAR MUMMUNAR AƘIDAR SHI'A A RIBAN GARMU DA SAURAN GARURUWANMU (1)

Lallai yazama dole muyi bayanin A kan illar wannan Addini na shi'a baya halatta yin shiru k**ar yanda Sheikh ibn bazz yafaɗa cikin Alfatawa nasa yace :

فلايجوز لأهل العلم السكوت وترك الكلام للفاجر والمبتدع والجاهل فإن هذا غلط عظيم ومن أسباب انتشار الشر والبدع واختفاء الخير وقلته وخفاء النسة ))
Ma'ana Baya halatta Ga Ma'abota ilimi yin shiru Akan Fajirai da Yan Bidi'ah da Jahilai, Domin yin Hakan sakachi ne mai Girma kuma Daliline na yaɗuwar Sharri da Bidi'ah, da Ɓoyuwar Alkhairee da Ƙaranchinsa, Da kuma Ɓoyuwar Sunnah.

To a ƙarƙashin wannan mukeso kusan cewa addinin shi'a yasaɓawa addinin sayyidina Aliyu (R) Domin Sayyidina Aliyu ya yadda da shigabancin Sayyidina Abubakar R. Amma Shi 'A basu yadda ba sam sam
MANZON ALLAH S.A.W DA KANSA YA UMARCI SAYYIDINA ABUBAKAR R.A YAYI LIMANCI MAGANA INGANTACIYYA DAGA BAKIN SAYYIDINA ALIYYU DAN ABI TALIB R.A

HAKA NAN MANZON ALLAH S.A.W YAYI SALLAH ABAYAN SAYYIDINA ABUBAKAR R.A

(1) RUWAYA TA FARKO: YAZO ACIKIN LITTAFI MAI SUNA "KITABUSH-SHARI,AH" NA BABBAN MALAMIN HADISIN NAN MUHAMMAD IBNUL HUSAIN WANDA AKAFI KIRA DA (AL-AJURRIY) AN HAIFESHI SHEKARA TA 264 bayan hijra, yau shekaru 1200 da wani abu kenan. Yace :

حدثنا أبو سعيد أحمد بن محمد بن زياد الأعرابي قال حدثنا إبراهيم بن فهد قال حدثنا محمد بن خالد الواسطي قال حدثنا شريك عن أبي بكر الهذلي عن الحسن قال: قال علي بن أبي طالب رضي الله عنه قدم رسول الله صلى الله عليه وسلم أبا بكر رضي الله عنه يصلي بالناس وقد رأى مكاني وما كنت غائبا ولا مريضا ولو أراد أن يقدمني لقدمني فرضينا لدنيانا من رضيه رسول الله صلى الله عليه وسلم لديننا
Duba Kitab Ash-Shari,ah na AL-AJURRIY wanda aka haifeshi 264 bayan hijra

FASSARA: Daga Alhassan dan Aliyyu dan Abi Talib, yace: ALIYYU BIN ABI TALIB yana cewa: " Annabi S.a.a.w ya gabatarda ABUBAKAR ALLAH YA KARA MASA YARDA akan ya Jagoranci Sallah ga Mutane, kuma alhalin Manzon Allah ya ganni awajen, kuma ban kasance bana wajen ba, haka nan ban kasance MARAS LAFIYA ba, da ace Manzon Allah yayi nufin ya gabatardani nayi limancin to da ya gabatarda ni, wannan yasa muka AMINCE MUKA YARDA da wanda Annabi s.a.w ya AMINCE YA YARDA dashi acikin addininmu, mu kuma sai muka YARDA dashi aduniyarmu (wato yana nufin ABUNAKAR R.A da kuma KHALIFANCINSA)" duba kitabushshari,ah na Al, Ajurriy, da Isnadinsa INGANTACCE k**ar yadda na kawo da larabci asama.

Wannan hadisi yazo daga bakin LIMAMAN DA 'YAN SHI,AH SUKE ƘARYAN CEWA NASUNE KUMA DUKKANSU MANYA MANYA HAR BIYU WATO ALHASSAN DA MAHAIFINSA ALIYYU R.A ALLAH YA KARA YARDA DASU.

MANZON ALLAH S.A.W YAYI SALLAH ABAYAN ABUBAKAR R.A

(2) HADISI INGANTACCE YA TABBATA ACIKIN LITTAFIN ALMUJTABA NA IMAM ANNASA,IY WANDA YA BAR DUNIYA 303 BAYAN HIJRA, KUMA NASIBAWA NE S**AYI SANADIYYAR MUTUWARSA, KUMA BABBAN MASOYI NE GA AHLUL BAITI, WANNAN YASA WASU SUKE JINGINA SHI'A GA SHI,ANCI GARESHI AMMA MAGANA CE MARAS MAK**A, MAGANA TA GASKIYA SHINE BA DAN SHI,AR RAFILAWA BANE!

BARI MUJE GA RIWAYAR:

عن أنس بن مالك رضي الله عنه قال: آخر صلاة صلاها رسول الله صلى الله عليه وسلم مع القوم خلف أبا بكر في ثوب متوشحا

MA'ana Anas bin Malik yace: " Sallar karshe da Manzon Allah s.a.w ya Sallata tareda Mutane ya Sallaceta ne abayan ABUBAKAR R.A....." duba ALMUJTABA NA IMAM ANNASA,IY haka nan IMAMU AHMAD CIKIN MUSNADINSA KARKASHIN HADISAN ANAS R.A

(3) HAKA NAN GA WATA RIWAYAR INGANTACCIYA:

عن الأسود عن عائشة رضي الله عنها قالت: صلى رسول الله صلى الله عليه وسلم خلف أبا بكر قاعدا في مرضه الذي مات فيه

Daga Aswad Almajirin Nana Aishatu r.a, daga ita Nana Aisha r.a ta ce: " Manzon Allah s.a.w yayi SALLAH abayan ABUBAKAR R.A azaune acikin rashin lafiyarsa da ya bar duniya acikinta" AL-IMAMU IBNU KATHIR BABBAN MALAMI MASANIN TARIHI DA HADISI DA TAFSIRI YAKE CEWA إسناده جيد ISNADIN WANNAN RIWAYA INGANTACCE NE duba littafinsa ALBIDAYA WAN-NIHAYA Juz,i na 5, shafi mai lamba 206.

HAKA NAN BABBAN MALAMIN NAN MASANIN HADISI DA FIQHU WATO IBNU ABDILBARRI WANDA AKA HAIFE SHI 368 bayan hijra YA NAQALTO ACIKIN SHARHINSA GA LITTAFIN MUWATTA,I MALIK DAGA IBNUL QASIM SHI KUMA DAGA IMAMU MALIK R.H

عن ابن القاسم عن مالك عن ربيعة ابن عبدالرحمن أن رسول الله صلى الله عليه وسلم خرج وهو مريض وأبو بكر يصلي بالناس فجلس إلى أبي بكر فكان أبو بكر هو الإمام وكان رسول الله صلى الله عليه وسلم يصلي بصلاة أبي بكر

Daga Ibnul Qasim, daga Malik r.h, daga babban malamin nan na garin madina alokacinsa RABI,ATU DAN ABDIRRAHMAN daga ANAS DAN MALIK yace: " Manzon Allah s.a.w ya fito alhalin baida lafiya, ga kuma Abubakar r.a yana LIMANCIN SALLAH ga Mutane sai Annabi s.a.w ya zauna kusa da Abubakar sai ABUBAKAR R.A YA KASANCE SHINE LIMAMI Manzon Allah yana yin Sallah da Sallar Abubakar.

WANNAN KADAN KENAN DAGA CIKIN RIWAYOYI INGANTATTU MASU YAWA DA S**A TABBATARDA CEWA ANNABI S.A.W YAYI SALLAH ABAYAN ABUBAKAR R.A.

AKWAI KUMA RIWAYOYI MASU YAWA WANDA DUK MAI KARATU YASAN DASU ,WANDA S**A TABBATARDA MANZON ALLAH YA UMARCI ABUBAKAR R.A YAYI LIMANCI GA SAHABBAI, K**AR YADDA YAKE CIKIN SAHIHUL BUKHARI DA MUSLIM DA MUWATTA,I MALIK DA SAURAN MANYAN LITTAFAN HADISAI MASU YAWA.

AMMA DA YAKE YAN SHI,AH MUGAYEN DAQIQAI NE, JAHILAI BASA KARATU SAI AKA SAMU SUNA KANTARA QARYAR BANZA WAI BA INDA YA INAGANTA AN UMARCI ABUBAKAR R.A YAYI LIMANCI, KAI KAJI JAHILCI D HAUKA!

TO MUJE MA AHAKA...! SHIN KUMA AKWAI INDA AKA UMARCI ALIYYU R.A YAYI LIMANCI???? IDAN KUN ISA KU KAWO MANA MU GANI, NI DAI GASHI NA KAWO MUKU.

DUK DA CEWA YAN SHI,AH SUNA JINGINA KANSU NE GA ALIYYU R.A, DOMIN SHI BAI SAN DA ZAMANSU BA, BAYA TAREDASU, ALIYYU R.A NAMU NE BA NASU BA! AMMA DUK DA HAKA NI ABDULHAMID IBRAHIM RG NA QALUBALANCESU SU KAWO WAJEN IDAN SUN ISA GA FILI GA MAI DOKI.

To Kunga Addinin Aliyyu ya sallama don haka namune Shukuma Addinin 'yan Shi'A Basu sallamaba don haka su bana nabane don muke ƙira da bannan murya 'yan uwanmu cewa kusani Addinin shi'A da ban islam da ban don haka kunesanci Shi'a Allah yakiyaye Ameeen

In sha Allahu fitowa tabiyu zamu bayyana rarrabuwan shi'a da aikinta na ta'addanci A cikin Al ummah ,,,

MU KYAUTATA AMFANI DA WAYOYIN MU !!!WAYA (Phone) ta zama wani jigo a rayuwar mutane na wannan zamanin. Ina ma ace yadda ...
02/10/2024

MU KYAUTATA AMFANI DA WAYOYIN MU !!!
WAYA (Phone) ta zama wani jigo a rayuwar mutane na wannan zamanin. Ina ma ace yadda mutane suke kusantar wayoyin su haka suke kusantar ALLAH da ambatonsa.
Haƙiƙa Waya tana daga cikin abubuwa da s**a fi rashin nauyi da sauƙin ɗauka anan Duniya... Domin idan ka dubi rayuwar al'ummah zaka ga cikin ƴan sakonni ko mintuna mutane basa iya jurewa ba tare da sun duba wayoyin su ba.
Sai dai kash !!! Ita wannan na'ura tana iya kasancewa mafi nauyin abubuwa da wahalar ɗauka a lahira ga duk wanda bai yi amfani da ita ta hanyar da ta dace ba. Domin yahudawa sun ƙirƙireta ta ne domin ta zama ma'abociyar shagaltar da mutane ga ƙauracewa abunda ke gaban su musamman na ibadah da kusantar Addininsu.
Sai dai baza su taɓa samun nasara ga ma'abota hankali da nitsuwa da hangen nesa ba, domin masu tunani suna shagala da wayoyin su ne ta hanyar ƙira zuwa ga addinin ALLAH (ﷻ) da sunnar Annabin Rahma (ﷺ)
Waya ta mallaki hanyoyi guda 2 sune: Alkhayri da Sharri.
Kuma haƙiƙa Magabata sun kasance:
ﻛﺎﻧﻮﺍ ﻳﺬﻛﺮﻭﻥ ﺍﻟﻠﻪ ﻗﻴﺎﻣﺎ ﻭﻗﻌﻮﺩﺍ ﻭﻋﻠﻰ ﺟﻨﻮﺑﻬﻢ
“Suna ambaton ALLAH a tsaye da zaune da kan kuiɓinsu”
Mu kuma yanzu muna jujjuya wayoyinmu a tsaye da zaune da kan kuiɓinmu !!!
Mu yi ƙoƙari mu yi amfani da wayoyinmu ta hanyar da ta dace domin duk abunda mu ka aikata da ita:
ﻛﻞ ﺃﻭﻵﺋﻚ ﻛﺎﻥ ﻋﻨﻪ ﻣﺴﺌﻮﻻ
Ya ALLAH k**ai damu zuwa gareka mai dawa mai kyau, ka sanya mu masu aikata alkhayri da wayoyin mu (Aameen)

ALHAMDULILLAHI NA KARƁI FAYAL NA K**A AIKI A OFISHINA A YAUKamar yanda sanarwa ta gabata tareda neman Addu'o'in daga bak...
20/09/2024

ALHAMDULILLAHI NA KARƁI FAYAL NA K**A AIKI A OFISHINA A YAU

Kamar yanda sanarwa ta gabata tareda neman Addu'o'in daga bakunanku masu Albarka tun ranan 03/RABI'UL AWWAL/1446 Wanda yayi dai dai da 06/SEPTEMBER /2024

Cewa nasamu kaina cikin jarabawan Shugabanci A Makaranta da nake karatu Don haka A tayani Addu'A

TO A AYAU 17/RABI'UL AWWAL/1446
20/SEPTEMBER/2024

Anbani Fayal na k**a Aiki gadan gadan in sha Allah A ofishina Anbani fayal A gaban Dukkan Patrol Naƙungiya Don haka Muna ƙara baran Addu'o'i daga gareku "yan uwa masu Albarka kusanyamu A Addu'A Allah yamana jagora

Ya ALLAH ka taimake mu akan dukkan abin da yafi ƙarfinmu, A wannan lamari da dukkan sauran Al'amuran rayuwarmu baki ɗaya domin lalle kai mai ƙarfi ne kuma mai jujjuya al'amurane ka juya kuskurenmu zuwa dai dai A wannan lamari.

Ya ALLAH ka shiryar damu bisa hanya madaidaiciya, hanyar Annabawa da salihan bayi, ka datar damu da abin da Ka halarta mana, ka nisantar damu da abinda ka haramta mana. A wannan dama daka bamu,

Ya ALLAH ka sanya mu cikin bayinka masu aikata alheri, bisa Wannan dama daka Bamu kuma kayi mana bushara da ayyukanmu na Alkhairi tun A nan duniya. Kayafe mana kurakuranmu.

Ya ALLAH Muna roƙonka shiriya da kamewa da Kuma wadatuwa.A Dukkan matan Rayuwa . Ya Allah Muna ƙara roƙonka Ka Amsamana Domin Lallai kai mai Amsawane,

(THIS IS FROM AMEEER ABDULHAMID IBRAHIM R_G 2024/2025 EXCOS)

(BAMBANCIN YAƘAR BIDI’A DA TSAURIN RA’AYI K**AR YADDA WASU "YAN UWA DA BASU FAHIMCEMUBA SUKE FAƊA A KANMU) Wasu mutane s...
20/09/2024

(BAMBANCIN YAƘAR BIDI’A DA TSAURIN RA’AYI K**AR YADDA WASU "YAN UWA DA BASU FAHIMCEMUBA SUKE FAƊA A KANMU)

Wasu mutane suna kasa bambancewa tsakanin yaƙar bidi’a da tsaurin ra’ayi. Shiyasa Alokacinda muke yaƙar bidi’a Sai su ɗauka cewa mu masu tsaurin ra’ayine A'A Wasu kuwa Suna kallon duk mai kira zuwa ga riƙo da Sunnah A jefar da bidi’a mai tsananin ra’ayi ne. Wannan zato tushensa shi ne rashin sani, da sauraron maƙiyan Musulunci, masu s**ar mabiyansa da cewa su masu tsananin ra’ayi ne.

Domin Riƙo da Sunnah da yaƙar bidi’afa shi ke tsare Musulunci daga lalacewa, da canjawa ta hanyar ƙari ko ragi, k**ar yadda tsoffin addinai s**a lalace, s**a canja. Addinin Musulunci shi ne addini na ƙarshe da Allah ya yi nufin ya wanzu k**ar yadda ya saukar da shi ba tare da sauyawa ba har zuwa ƙarshen zamani. Don haka Allah ya tanadi wasu matakai na tsare shi da kiyaye shi don kada ya canja ko ya sauya. Daga cikin waɗan nan matakai akwai tsare littafin Musulunci, Alƙur’ani, daga sauyawa k**ar yadda aka sauya Attaura da Linjila, da tsare Sunnah wacce ita ce fassarar Alƙur’ani a aikace daga gurɓacewa.

Allah Maɗaukaki ya ɗauki nauyin tsare Alƙur’ani shi da kansa, k**ar yadda ya ce, (“Lalle mu ne muka saukar da Ambato (Alƙur’ani), kuma lalle mu, haƙiƙa, masu kiyayewa ne gare shi.” (Suratul Hijr: 9). Haka nan, ya tsare Sunnah ta hanyar umarni da riƙo da Sunnah da yaƙar bidi’a a bisa harshen Manzonsa, k**ar yadda muke karantawa a cikin hadisai ingantattu.

Saboda haka, "yan uwa masu mana wannan kallon munaso kusani cewa, masu yaƙar bidi’a suna bin umarnin Manzon Allah ne, ba wani abu sabo suke ƙirƙira ba. Su masu gadin Musulunci ne, masu tsare shi daga lalacewa k**ar yadda tsoffin addinai s**a lalace. Ba don aikin masu yaƙar bidi’a ba da yanzu Musulunci ya zama k**ar Kiristanci, babu abinda zai rage a cikinsa sai sunansa kawai. Shi ya sa yaƙar bidi’a ya zama mafi girman ibada, sama da ibadojin nafila da yaƙin jihadi, k**ar yadda magabatan al’umma na ƙwarai s**a tabbatar. A littafafensi,

"Yan uwa kusanifa Bidi’a tana Rusa Duniya da Addini:
Ma’anar bidi’a, k**ar yadda muka gani a littafafen, magabata ita ce, “Ƙagar wani abu a cikin addini wanda ya yi k**a da addinin, amma ba ya cikin addini. Hujjah A duba koda Ihya’us SunnaH wa Ikhmadul Bidi’a na Shehu Usmanu Danfodiyo, bugun Darul Fikir, Bairut, 1962, shafi na 22]. Wannan yana nufin bidi’a algus ce a cikin addini, Don Wannan kenan fita ta farko in Sha Allahu Tabiyu nazuwa bada jimawa

Kuma munanan A kan Cewa Maulidi Ba islam bane Allah yashirya Ameeeeen

WARWARE SHUBUHAR MASU MAULIDI A KAN SALLAH DA SIFIƘA DA FANKA DA SHINFIƊI (003)06/RABI'UL AWWAL/ 144609/SEPTEMBER/2024YA...
09/09/2024

WARWARE SHUBUHAR MASU MAULIDI A KAN SALLAH DA SIFIƘA DA FANKA DA SHINFIƊI (003)

06/RABI'UL AWWAL/ 1446
09/SEPTEMBER/2024

YANA DAGA CIKIN SHUBUHAR SU CEWA TO IN KUNCE MAULIDI BID'ANE To SHIN KIRAN SALLA DA AMSA KUWWA WATO (LOUDSPEAKER) KO
SALLA DA ITA A MASALLACI BID'A NE?
AMSA: A'A ba Bidi'a bane halataccen Aiki ne
Dalili:
عن ميمونة قالت: كان النبي صلى هللا عليه وسلم يصلي على الخُمْرة. متفق عليه
Nana Maimuna Radiyallahu Anha ta ce: Manzon Allah Sallalahu
صلى الله عليه وسلم ya kasance yanayi salla aka Khumra (kan wata yar ƙaramar
shimfiɗa da ake sawa domin kare kai daga ƙasa yayin sujjada)
Bukhari Da Muslim
Daga Hadisin nan zamu fahimci ashe ya halatta yin amfani da
abubuwan da s**a halatta wajan yin Ibaadu.
Dukkan Abinda Allah ya halitta a Duniyan nan yace dan mu yayi
yishi
هو الذي خلق لكم ما في اْلرض جميعا
Komai halal ne muyi amfani dashi sai abunda Allah ya haramta
na abubuwan rayuwa.
Abinda ya shafi ibada kuwa ko wacce haram ce sai wadda akace
ayi.
Yin salla da sfika ko fanka ko shimfiɗa duk ababe ne na rayuwa
nassi baizo da cewa kar ai amfani dasu ba, saboda haka ya halatta,,

Yin amfani dasu matuƙar babu Almubazzaranci, sannan abunda
ya shafi sfika matuƙar ba shiga haƙƙin Al'ummah musamman
sallar dare, wannan duk ya halatta.
Akwai ababen amfani na rayuwa da nassi yazo kansu, misali
Carbi wajan zikiri, Manzon Allah صلى الله عليه وسلم yace ayi da yatsu, Shiyasa har
malamai s**ai saɓani shin hani yayi kar ayi da komai sai yatsu
kokuwa falalar yi da yatsu ya ambata, duk da saɓanin da akai
mafi kyau da dacewa da sunna shine ayi da yatsu tunda shi haka
yake yi kuma yace ayi, Kuma hakan ke nuna carbi bashi da wata
falala k**ar yadda fankar masallaci bata da falala kawai ababen
amfani ne saidai shi carbin ma ba'a san ƙidaya zikiri dashi sai dai yatsu,

Fahimtar asalin wani aiki a shari'ar Musulunci shi zai taimaka ma
mutum wajan banbance menene Bid'ah da mene ba Bidi'ah ba
shiyasa abun ya bani mamaki matuƙa da naga wasu na iƙrarin
wasu ayyuka Bid'a ne saboda suna son kare ra'ayinsu na Maulidi,
sun ɗauka komai sai an faɗe shi a Hadisi ko Aya shine yake daidai
a Addini, akwai abubuwan da da yawa ba ai magana kansu ba
amma akwai asalin su a shari'ar Musulunci kuma akansu ake
gina su, karatun Usulul Fiƙhi zai taimaka ma mutum sosai wajan
fayyacewa.
Ƙiyasta halattun ayyuka da Maulidi ba abinda ke kawo shi sai
ƙarancin ilimi, domin Maulidi aiki ne dake tattare da ibadar son
Manzon Allah صلى الله عليه وسلم, kuma ita Ibada sai yadda akace ayi za ai, babu
shakka sahabbai sun fi mu son Manzon Allah صلى الله عليه وسلم sai mu koma
muga me s**ayi, me ya yarje musu suyi da sunan sonsa?
Sannan asalin aikin yadda nasha bayani aiki ne mai rusashen
asali (ko wace idi an soke ta sai idi babba da ƙarama) sannan bata
da wani aiki da zaka jona ta tare dashi ta samu wajan zama a
Musulunci.
Allah ya bamu kyakkyawan fahimtar Addininmu,

Ya ALLAH Haƙiƙa Mun shaida Kai ne Ubangijinmu, kuma Musulunci shi ne Addininmu, Kuma Muhammad (ﷺ) shi ne Manzonmu don haka munaroƙonka kabamu ikon yin Addininka yanda Annabinka (ص) yakoyar kuma ka datar damu da mafi dacewa a duniya da lahira. Ameeeeeeen ya Allah

NAUYI KAN NAUYI "YAN UWA KUSA ƊAN UWANKU CIKIN ADDU'O'INKU WATO ( ABDUL HAMID IBRAHIM  R_G) JIYA ASSABAR WANDA YAYI DAI ...
08/09/2024

NAUYI KAN NAUYI "YAN UWA KUSA ƊAN UWANKU CIKIN ADDU'O'INKU WATO ( ABDUL HAMID IBRAHIM R_G)

JIYA ASSABAR WANDA YAYI DAI DAI DA 03/RABI'UL AWWAL/1446
06/SEPTEMBER/2024 MUNZIYARCI WAJEN HANDILIN OVER NA ƘUNGIYAR J.B.W.I.S WANDA TUNTUNI NAKE MEMBER A CIKINTER TSAKANIN TSUFFIN ƊALUBAI DA SABI KAWAI MUNA ZAINE BAYAN KAMMALA BASU CERTIFICATE ANZO ZA'A ZAYYANA SABBIN SHUGABANNI KAWAI SAI NAJI AN AMBACI SUNANANA A MATSAYIN SABON SHUGABA (AMEEER) J.B.W.I.S. DA WANNAN NAKE ROKONKU "YAN UWA MA SU ALBARKA KUTAYAMU ADDU'A

YA ALLAH KABAMU IKON CIKA ABUBUWA SHABIYU WANDA SUKEKANGA JAGORANCI NA GARI K**AR YANDA WASU CIKIN MALAMAN MUSLUNCI S**AFAƊA.

Wanda Sune k**anr haka (Tsoran Allah da ganin girman sa. Ilmi da sani mak**ar aiki. Adalci, Tausayi, Rikon Amana, Cika alƙawari, Gaskiya, Iya aiki da ƙwarewa.Wayewa da sanin halin jama'a.da hangan nesa.)

Siffofi goma sha biyu kenan na jagoranci nagari Ya Allah karka barmu da wayonmu Kadafamana Ka taimakemu da taimakonka ka yafemana A inda mukakuskure Ya Allah.

WARWARE SHUBUHAR MASU MAULIDI A KAN TAFSEER NA ALƘUR'ARNI CIKIN RAMADAN (002)SHIN TAFSIRI A WATAN RAMADAN YANA DA ASALI ...
06/09/2024

WARWARE SHUBUHAR MASU MAULIDI A KAN TAFSEER NA ALƘUR'ARNI CIKIN RAMADAN (002)

SHIN TAFSIRI A WATAN RAMADAN YANA DA ASALI A
MUSULUNCI?
AMSA: E!
Dalilai:
1. Cikin Hadisi na 2699 Da Imam Muslim ya fitar:
Manzon Allah صلى الله عليه وسلم ya ce: wasu mutane bazasu taru ba cikin wani
gida daga gidajen Allah (masallatai) suna tilawar littafin Allah,
Suna Mudaarasar sa tsakanin su, face nutsuwa ta sauka garesu,
rahama ta lulluɓe su, Mala'iku sun kewaye su....
Bisa wannan Hadisi zamu fahimci cewa Haɗuwa a masallaci ai
tilawar Alƙur'ani aiki ne mai falala saidai Malamai s**ace ana
nufin bawai biyawa tare ba da murya ɗaya, ko dai kowa ya biya
nasa, ko ɗaya ya biya sauran suna sauraro k**ar yadda aka samu
sahabbai suna yi, haɗuwa a biya da murya ɗaya wannan ya saɓa
ma Ayar Alƙur'ani da Allah ke bayanin cewa in ana karatun
Ƙur'ani ayi shiru a saurara (A'araf 204) sai dai malamai sunce
babu laifi wajan koya ma yara Ƙur’ani malami ya biya sannan Ɗalubai subiya da murya ɗaya

Mudarasar Alƙur'ani kuwa malamai s**a ce shine tadabburin sa,
fahimtar sa, ciro fa'idoji, tsayar da haddar sa, tsayar da tajweedi
da sauran su.
Kunga kenan zama a Masallaci ayi Tafsirin Alƙur'ani na
ƙarƙashin wannan aikin falala.
Wani zaice meyisa a Ramadan aka fi yi?
Amsa: Ya tabbata a Hadisi a Bukhari Da Muslim Daga Abdullahi
Bin Abbas cikin Hadisin daya rawaito yake cewa Mala'ika Jibril
yana zuwa ma Annabi صلى الله عليه وسلم duk dare na Ramadan yai masa
Mudarasar Alƙur'ani.
Wani Hadisin Na Muslim (2450)
Hadisin da Nana Aisha Radiyallahu Anha ta rawaito daga Nana
faɗima take cewa Manzon Allah صلى الله عليه وسلم ya ce mata Mala'ika Jibril yana
zuwa mun duk shekara Mu'aradar Ƙur'ani sau ɗaya ko biyu
(ruwayar Bukhari ta tabbatar sau ɗaya ne) amma wannan
shekarar yazo mun sau biyu ni ina ganin Ajali nane ya kusa...
Ibn Kasir Cikin Tafseerin sa (1/ 51).
Yake bayanin mene Mu'arada, ya ce shine zuwa da yake tabbatar
ma Manzon Allah صلى الله عليه وسلم abinda akai masa na wahayi a shekarar da
Muƙabalar haddar da tabbatar da abinda ya tabbata da shafe
abunda aka shafe na ayoyi, yace a cikin Watanni kuma a
Ramadan suke yi saboda cikin sa aka saukar da Alƙur'ani

Shima zamu cigaba nagaba zamu warwaare shubaharsu A kan lasiƙa da fanka A masallatai in sha Allah

LOKACIN AMSAR ADDU'A RANAR JUMA'A !!!Hadisai sun tabbatar da cewa akwai lokacin da ALLAH (ﷻ) Ya ke amsawa bawa idan yayi...
06/09/2024

LOKACIN AMSAR ADDU'A RANAR JUMA'A !!!
Hadisai sun tabbatar da cewa akwai lokacin da ALLAH (ﷻ) Ya ke amsawa bawa idan yayi addu'a a ranar juma'a.
An Karɓo Daga Abi Hurairah (Ra) Ya ce: Manzon ALLAH (ﷺ) Ya ce: “lalle a ranar juma'a akwai wani lokaci, wanda babu wani mutum musulmi da zai tsaya acikinta yana roƙon ALLAH face ALLAH ya biya masa buƙatar sa“ Ya na misalta ƙarancin lokacin da hannun sa (ma'ana lokacin bashi da yawa).” [Sunan Ibn Majah: 1191]
A wata ruwayar ya ce: lokacin shine yanki na ƙarshen wuni.
Malamai sun samu saɓani game da wannan lokaci, amma mafi rinjaye shi ne magana guda biyu: Daga hawan liman kan mimbari zuwa ƙare sallah, sannan kuma daga bayan sallar La'asar zuwa faɗuwar rana, kuma wannan shi ne magana mafi inganci k**ar yadda yazo acikin [Zaadul Ma'aad: 1/377]
Ribatar lokacin amsar addu'a a ranar Juma'a yana da matuƙar muhimmancin tsayawa da yawaita addu'a a bayan sallar La'asar ranar juma'a k**ar yadda hadisin ya rinjayar da amsar addu'ar a bayan sallar La'asar.
Manzon ALLAH (ﷺ)Ya ce: “Ranar Juma'a awa goma sha biyu ce, ba a samu wani Bawa musulmi ba, da ya roƙi ALLAH (ﷻ) wani abu ba, face sai an ba shi wannan abun da ya roƙa, A nemeta (Lokacin karɓar Addu'ar) a ƙarshen sa'ar bayan sallar La'asar.” [Imam Albany ya inganta shi]
Sheikh Ibn Bazz (Rahimahullah) Ya ce: “Wannan lokacin shi ne bayan sallar la'asar har zuwa faɗuwar rana ga wanda ya zauna ya na jiran sallar magariba, a masallaci ne ko a gida, mace ne ko namiji ya zauna yana jiran lokacin amsar addu'a, sai dai namiji ba zai yi sallar magariba a gida ba ko ma sauran salloli (na farillah) face da wani uzuri da shari'a ta yarda dashi...” [Majmu'ul Fatawa wa muƙalaat Sheikh Ibn Baaz: 6/159]
ALLAH Ya sa mu dace (Aameen)

BABU BIKIN MAULIDI A MUSULUNCI (005) (03/RABI'UL AWWAL/144606/SEPTEMBER /2024 Abdulhamid ibrahim (R_G) Dukkan wanda zai ...
06/09/2024

BABU BIKIN MAULIDI A MUSULUNCI (005)

(03/RABI'UL AWWAL/1446
06/SEPTEMBER /2024

Abdulhamid ibrahim (R_G) Dukkan wanda zai yi Comments to don Allah kafara karanta na 1,2,3,4, domin wannan na biyarne kuma na shida yana zuwa in sha Allah

Wani yace: kaduba yawan masu maulidi Amma kace : ba islam bane nace: baya halatta ga mai hankali yaruɗu da yawan masu aikatashi na sauran mutane A sauran guran gurare, domin ita gaskiya ba a saninta ta hanyar yawa A'A ana saninta ne kawai da hujjojin Shari'a k**ar yadda Allah Ta'ala yace: yahuduwa da sarawa (Sukace babu wanda zai shiga Aljannah face wanda ya kasance bayahude ko banasare. Sai Allah yace: wadannan burace buracensune, kawai kace ku kawo hujjojin idan kun kasance masu gaskiya ) Kuma Allah Ta'ala yace (idan kuka bi mafiya yawan waɗanda suke bayan ƙasa to zasu ɓatar da kune. ) kaga yin hujja da cewa suna da yawa bai tasoba Sa'annan bayan kasan cewar wannan maulidai bid'ane basa kuɓuta daga wasu munanan Abubuwa wasu lokutan a wasu guraran, k**ar cuɗanya maza da mata da sauraren waƙoƙi da ƙide-ƙide da bushe-bushe da shan muyagun ƙwayoyi, da wanin waɗannan na sharri . Da kuma abin da yafi wannan muni ma yana iya aukuwa shine Shirka mafi girma, wannan kuwa yana faruwa kan zurfafawa kan manzan Allah (S.A.W) ko waninsa na waliyai da rokonsa da neman Agajinsa da neman karin ni'ima daga gare shi Tare da kudurcewa lallai shi Waliyin ya san gaibi da mak**ancin haka na Al'amurorin da suke kafurta mai aikata su. Kuma haƙiƙa hadisi ya inganta daga manzan Allah (S.A.W) Cewa lallai shi yace ( ina gargaɗin ku kada ku zurfafa cikin Addini, domin babu abinda ya hallakar da waɗanda suke gabanin ku face zurfafawa cikin Addini)

Kuma manzan Allah (S.A.W.) yace : (kada ku zurfafa wajen garmamani k**ar yadda nasara s**a zurfafa wajen girmama ɗan maryama, ni bawane kawai kuce bawan Allah kuma manzansa,) Bukhari ya ruwaito shi, kuma yana cikin Abin ban mamaki da Al'ajabi shine wasu mutane suna bayar da himma da ƙoƙari wajen halartashi (Wannan Maulidan bid'ar) kuma suna kare duk wani s**a kan maulidin kuma suna kauracewa abin da Allah yace ayi na halartar Sallar Jumma'a da Sallar Jama'i A ranan maulidai Amma basa damuwa da hakan basa ganin cewa sun yi wani mummunan abu mai girma wannan babu shakka yana daga cikin rauni imani ne da karancin basira da yawan Abin da yayi tsatsa na nau'in zunubai da saɓo, muna rokon Allah ya sawwaƙe mana da dukkan sauran musulmai Ameeeeeen

Zamu tsaya Anan Amma zamu cigaba in sha Allah in wannan Shine karan tawanka na farko kanemi 1,2,3,4, domin wannan na biyar ne kuma nashida yana zuwa in sha Allah Ya Allah kasa mu dace da dai dai Ameeeeeen

BABU BIKIN MAULIDI A MUSULUNCI (004) (02/RABI'UL AWWAL/144605/SEPTEMBER/2024)Abdulhamid ibrahim (R_G) Dukkan wanda zai y...
05/09/2024

BABU BIKIN MAULIDI A MUSULUNCI (004)

(02/RABI'UL AWWAL/1446
05/SEPTEMBER/2024)

Abdulhamid ibrahim (R_G) Dukkan wanda zai yi Comments to don Allah kafara karanta nafarko, da nabiyu da na uku domin wannan na huɗune kuma in sha Allahu na biyar yana zuwa da ikon Allah,

Kuma Allah Ta'ala yace : (Kowane Abu kuka yi jayayyah a kansa to hukuncinsa yana ga Allah) to idan mun mayarda da wannan matsar itace matsalar maulidi misali mun mayar da ita zuwa ittafin Allah sai mu samu yana yi mana umarni da bin Abin da manzon Allah yazo dashi, kuma yana bamu labarin cewa lallai Allah Subhanahu ya cikawa wannan Al'umma addininta kuma wannan Maulidin baya cikin Abinda manzan Allah yazo dashi, sai ya kasance baya cikin addinin da Allah ya cika mana kuma idan mun mayar da ita zuwa hadisai manzon Allah bazamu samu ya aikata shi ba, kuma bai yi umarni da shi ba, kuma sahabbansa ba suyi shi ba, (R.) Da hakane muke sanin cewa baya cikin Addini, sam sam Amma cikin bid'a fararriya, kuma da yin k**a Ahlul kitab wato yahudawa da nasarawa cikin idinansu (Sallolinsu.) da haka yake kara bayyana ga kowane mai ƙaramar basira da kwaɗayin gaskiya da kuma Adalci wajen neman gaskiya cewa lallai dukkan Maulidai ba sa cikin addinin musulunci cikin komai : yana cikin fararrun Al'amurane , waɗanda Allah Subhanahu da manzonsa Sukayi maganar gargaɗin cewa mu nisance su kuma mu gujesu watau Dukkan Maulidannan,

Don haka zamu tsaya A nan ƙarshen na huɗu na biyar yana zuwa in sha Allah don haka in wannan shine farkon karatawanka to ina baka Shawari kaje baya ka karanta Sauran kafin yin hukunci Allah yasa Mudace Ameeeen

Address

006
Kirfin Kasa
NIL

Telephone

+2348145009754

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Jibwis RIBAN GARMU posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Contact The University

Send a message to Jibwis RIBAN GARMU:

Share