07/01/2023
An samu hatsaniya a lokacin Sallar Juma'a a Masallacin Izala da ke Kano saboda rikicin Limanci
Rigima kan shugabanci a Masallacin Darul Hadith na marigayi Sheikh Dakta Ahmad Ibrahim BUK dake Tudun Yola a Kano, ta kawo tsaiko yayin gudanar da Sallar Jumu'a ranar 6 ga watan Janairu, 2023.
Jaridar Daily Trust ta rahoto cewa rigimar ta ɓarke ne lokacin da wasu daga cikin manyan Masallacin s**a hana sabon Limami wucewa, yayin da zai shiga ya hau Mimbari don jagorantar Sallar Jumu'a.
Wasu bayanai da ake yaɗa wa sun nuna cewa fusatattun mutanen sun hana Limamin hawa Mimbari ya yi huduba, lamarin da ya kawo tsaiko yayin Sallar mai dumbin falala.
Limamin, wanda aka tsara zai jagoranci Sallar a jiya, ya k**a hanyar shiga wajen da aka ware wa Liman a Masallacin, ba zato mutanen s**a tare shi, an ce har rigarsa s**a rike.
Sak**akon wannan takaddama da aka samu, nan take jami'an tsaro s**a shiga tsakani, s**a kewaye Masallacin don tabbatar da doka da oda, hakan ya sa wasu Masallatan s**a k**a gabansu.
Da yake tabbatar da faruwar lamarin, mai magana da yawun rundunar 'yan sanda ta jihar Kano, Abdullahi Haruna Kiyawa, yace ba tare da bata lokaci dakarun 'yan sanda s**a kai ɗauki bayan samun kishin-kishin din abinda ke faruwa.
"Nan take Kwamishinan yan sanda ya umarci a tura karin jami'ai Masallacin domin tabbatar da bin doka da oda." "Jami'an sun dawo da komai kan hanya kuma an gudanar da Sallah ba tare da wata matsala ba.
A halin yanzun hukumar 'yan sanda ta gayyace bangarorin biyu domin gano bakin zaren." - Abdullahi Kiyawa.
Tuni dai mazauna yankin Amguwar Tudun Yola s**a ci gaba da harkokin gabansu bayan abinda ya faru a Masallacin.