Barrister Rabiu Adam Fulani Katsina

Barrister Rabiu Adam Fulani Katsina Injustice to one means injustice to all, as he said not as i means.

06/02/2022
04/02/2022
01/02/2022

Lokacin juyin mulki ya wuce a Nijeriya, in ji Buhari

Shugaban Ƙasa Muhammadu Buhari ya ce ba za a sake yin juyin mulki na sojoji a Nijeriya ba.

Buhari ya faɗi hakan ne a wani martani kan damuwar da gwamnan Jihar Ekiti, Kayode Fayemi ya nuna kan guguwar juyin mulki da ta taso a Afirka da ta haɗa da hamɓare gwamnatocin domokraɗiyya a Mali, Guinea da Burkina Faso.

Kamfamin Daillancin Labarai na Ƙasa, NAN ya rawaito cewa Buhari ya ce ya na da ƙarfin yaƙinin cewa Nijeriya ta wuce lokacin yin juyin mulki.

Buhari ya baiyana haka ne a wata liyafa da kwamitin ƴan siyasa, ƴan kasuwa, ƴan jarida da ƙungiyoyi masu zaman kansu su ka haɗa a fadar shugaba kasa a jiya Litinin.

A watan Nuwambar 2021 ne Buhari, tsohon shugaban ƙasa na mulkin soji, ya jaddada cewa Afirka ba za ta lamunci juyin mulki ba bayan da a ka yi juyin mulki a Guinea da Mali.

01/02/2022
01/02/2022

Shugaban Amurka Joe Biden ya ce nan ba da jimawa ba zai aike da wasu Karin adadin sojojin Amurka zuwa Gabashin Turai domin karfafa rundunar tsaro ta NATO a daidai lokacin da takun saka ke karuwa kan…

01/02/2022
01/02/2022

LABARAI DA DUMI-DUMIN SU!

Yanzu haka da rana tsaka 'yan bindiga sun afkawa garin Rarah dake cikin karamar hukumar Rabah jihar Sokoto suna harbe-harbe

Rahotanni da ke zuwa mana yanzu haka sun tabbatar da cewa 'yan bindiga sun afkawa garin Rarah da ke cikin karamar hukumar Rabah jihar Sokoto.

Wani dan garin Malam Haliru Ibrahim Rarah ya shaidawa jaridar Nasara cewa yanzu haka suna can suna harbe-harbe cikin garin.

Nasara
Media News

01/02/2022
01/02/2022

Duk Wanda Zai Gajeni Zai Kwashi Garaɓasar Gyararriyar Kasa Da Haɓɓakar Tsaro, Cewar Shugaban Kasa Muhammadu Buhari

Rahoton Daily Nigerian Hausa

Shugaban Kasa Muhammadu Buhari ya yi alƙawarin bar wa magajin sa gyararriyar ƙasa mai cike da haɓɓakar noma, tattalin arziki, cigaban dimokaraɗiyya da kuma haɓɓakar tsaro.

Buhari ya baiyana haka ne a wata liyafa da kwamitin ƴan siyasa, ƴan kasuwa, ƴan jarida da ƙungiyoyi masu zaman kansu su ka haɗa a fadar shugaba kasa a jiya Litinin.

Buhari ya ce yana ƙoƙarin ya bar mulki a 2023 gami da miƙawa magajinsa ƙasa mai cike da haɗin kai, zaman lafiya da ci gaba a shekaru 24 na mulkin dimokuraɗiyya ba tare da samun cikas ba.

Ya ce ƴan kasuwa maza da mata za su samu haɓɓakar kasuwanci da tattalin arziki.

Ya kuma baiyana jin daɗin sa na yadda ƴan bokon ƙasar nan su ka gane cewa gyaran ƙasar hakki ne a kan kowa da kowa.

Buhari ya ƙara da cewa akwai aiki ja a gaban ƴan ƙasa wajen gyaran ƙasar, inda ya baiyana ƙwarin gwiwa cewa gyaran ba zai gagari gwamnati da al'umma ba.

Masu karatu me zakuce?

01/02/2022

Address

Wuse Zone 2
Abuja

Telephone

+918107107312

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Barrister Rabiu Adam Fulani Katsina posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share