11/10/2024
WATA SABUWA: Babbar kotun tarayya da ke Abuja ta bayar da umarnin hana kwamitin zartarwa na kasa (NEC) da kwamitin amintattu na jam’iyyar PDP korar Umar Damagum daga mukaminsa na shugaban riko na jam’iyyar PDP
A yau Juma'a ne Jaridar ATP Hausa ta rawaito cewa, Masu ruwa da tsaki na jihar Ribas sun dakatar da shugaban jam'iyyar PDP na kasa da sakataren jam'iyyar na kasa bayan zarginsu da raba kafa.
An yanke wannan huluncin ne a wata tattaunawa da mambobin su gudanar a babban birnin tarayya Abuja a safiyar yau Juma’a.
Sakataren yada labarai na jam’iyyar na kasa, Debo Ologunagba, ne ya tabbatar da hakan. Ya fitar da sanarwar da ke isar da hukuncin NWC da karfe 3:18 na safiyar yau Juma’a.
Sanarwar ta ci gaba da cewa: “Kwamitin ayyuka na kasa, NWC, na jam’iyyar PDP ya yi nazari sosai kan jerin korafe-korafen da aka yi wa shugaban riko na kasa, Amb. Illiya Damagum da Sakatare na kasa, Sanata Samuel Anyanwu, musamman dangane da wasikar da s**a aike wa kotun daukaka kara a kan matsayin jam’iyyar a shari’ar da ta shafi tsaffin ‘yan majalisar dokokin jihar Ribas su 27, wadanda s**a bar kujerunsu. Bayan ya sauya sheka daga PDP zuwa APC.
Sai dai babban Kotun Tarayya dake Abuja ta hana cire Shugaban rikon Iliya Damagum akan mukaminsa na shugaban riko.