30/11/2021
Da GASKE Ka KE KO YAUDARAR KANKA Ka KE??
Imam Ibnul Jauzi Allah ya masa rahama yana cewa, "Sau tari akan samu mutum yana ikrarin yana da tauhidi alhali mushrikine wa Ubangijinsa, dayawa akan samu mai cewa shi bawan Allah ne alhali kuma bawan cikinsa ne, yana saɓawa Ubangijinsa wurin yiwa kansa biyayya, ya sayar da yardar Allah dan neman yardar abun halitta irinsa.
Sau nawa aka samu mai bin son zuciyarsa wanda ya riki zuciyarsa a matsayin abun bautarsa, sau nawa kuma aka samu wanda yayi riko da umarnin Ubangijinsa wanda yake sayar da kansa wurin neman yardar Ubangijinsa".