21/09/2021
mijin tace*7*
nan,kai
ne farkon wanda zan gayawa ba shi alh ba.
Ina bin umarni naka ne k**ar yanda nake bin na
baba da ya hana ni fitar da Fadima daga dakinta
ba da izinin mijinta ba.ya gyada kai alamar
gamsuwa d maganar tata Kafin ya tambaye abin
da ya sake faruwa, ta ce "eh to ni kam bansan
komai ba tunda baya kai kara kan laifukan da ake
yi mishin, sai dai yayi hukunci na ganin dama
saboda ganin komai yayi ana sharewa.in banda
haka me fadima zata yi wa mutumi yayi mata iri
abinda ake yi mata a gidan nan. Nan da nan ta
shiga share hawaye tana fadin a rokan man shi
kawai ya bani ita muji gida, inna yi jinyarta ta
warke musan abin da muke ciki.Haj shi babba fa
da hakuri aka san shi,kin kuma sani sarai ita
mace komai gatanta bata da wata darajar da ta
wuce dakin aurenta.tace "haka ne" ya ce to ina
dalilin komai kankantar abinda ya faru a gidan
nan baza kubar maganar a tsakaninsu ba sai kun
shiga?sai kuyiwo gayya ku cika mishi gida? Ita
Gambo bata laifi ne ? Kuma don yar gata ce a
danginta da ke da Alh Maikudi sai ace ba shi da
iko a kanta .Haj Kubra ta soma kuka tana fyace
majina tace in tayi laifi sai ayi mata duka har
targade?kuma menene laifin taki yiwa matarshi
aiki?mai aiki na kawo mata ne?Inna Hajara taleko
ta na sannu da zuwa Mallam,ya na daga ido ya
kalle ta yace ia kuma duk kunzo ne kuna ciki?to
duk ko fito koma ciki ki gaya musu nace duk ku
fito ku bar gidan.in na bar nan kuma zan je in
gaya wa mallam har da ku a rura wutar fitinar
dake aukuwa a gidan nan.nan da nan s**a fito
suna tafiya soboda sanin matsayin baba yahaya
wurin Mal mai babban allo,matsayin da tuni ya
maida shi yazama dagida.yatsaya har s**a gama
wucewa ya kalli H.kubra ya ce haj kiyi hakuri kiyi
hakuri na roke ki kar kije ki ce zaki gayawa wa
Alh Maikudi munin Al'amarin tunda shi ma bai
san hakuri ba.