Tunatarwa A Shari'ar Muslunci

Tunatarwa A Shari'ar Muslunci ٱه‍دنا الصراط المستقيم

27/11/2025

MUTUWA!

Yau wane ya mutu gobe wane ya mutu jibi ma haka kullum ma haka amma mutuwa bata zaman mana wa'azi, daga an faɗa mana Sai muce Allah ya jikansa ya gafarta masa Amma kuma baza mu wa'azantu da wannan mutuwar bah.
kamata yayi idan muka ga anyi mutawa sai mu ƙara gyara tsakanin mu da Allah sannan mu tuna cewar muma muna nan tafe.

Allah yasa muyi kyakkyawan ƙarshen 🤲

Allah ya Jiƙan Sheikh Ɗahiru Usman Bauchi, Allah ya gafarta masa damu baki daya 🤲

15/11/2025

Enjoy the videos and music you love, upload original content, and share it all with friends, family, and the world on YouTube.

15/11/2025
02/10/2025

Mafificiyar Sallah inji Annabi Muhammad صلى الله عليه وسلم itace sallar asuba ranar Jumu'a acikin jam'i

📚 Ibn Khuzaymah a cikin Sahih (no. 1734)
📚 Al-Bayhaqi a cikin Shu’ab al-Iman (no. 2773)
📚 Al-Tabarani a cikin Al-Mu’jam al-Awsat (no. 6550)

نص الحديث:قال رسول الله صلى الله عليه وسلم:«أحبُّ الصيامِ إلى الله صيامُ داودَ، كان يصومُ يوماً ويُفطرُ يوماً»Fassara:Ma...
16/09/2025

نص الحديث:
قال رسول الله صلى الله عليه وسلم:
«أحبُّ الصيامِ إلى الله صيامُ داودَ، كان يصومُ يوماً ويُفطرُ يوماً»

Fassara:
Manzon Allah (ﷺ) ya ce:
“Mafi soyuwan azumi a wurin Allah shi ne azumin Dawuda (A.S). Yana yin azumi rana guda, sai ya karya a rana guda.”

Wannan hadisin yana nuna:

Mafi falalar azumi na nafila shi ne yin azumin Annabi Dawuda, wato yin azumi a rana, sai a huta a rana.

Wannan hanya tana kiyaye mutum daga gajiya, tana kuma tabbatar da daidaito tsakanin bautar Allah da hakkokin jiki.

Takaitawa:
Azumin Annabi Dawuda (A.S) shine mafi alheri a azumin nafila, saboda haka ma'aiki Sallallahu alaihi Wasallam ya faɗa.

📚 Hadisin yana cikin Sahih al-Bukhari (3420) da Sahih Muslim (1159).

14/09/2025

Sai mai Hankali ne kawai zai Fahimci hakan

12/09/2025

"Duk wanda ya karanta Suratul Kahfi ranar Juma'a, za'a saukar da wani haske zuwa gare shi, zai kasance a tare dashi har zuwa wata Juma'ar da zata zo".
🎤:
Inji mai-gidan mu, annabi Muhammad (S.A.W).
Karanta littafin "At-targiybu Wat Tarhiyb", A Volume na daya shafi na 298.

12/09/2025
12/09/2025

FALALAR KARATUN SURATUL KAHFI

1. Kariyar daga Dajjal

Annabi ﷺ ya ce:

“Duk wanda ya haddace ayoyi goma na farkon Suratul Kahfi, zai sami kariya daga Dajjal.”
(Muslim ne ya rawaito).

A wani riwayar kuma:

“Duk wanda ya karanta farkon Suratul Kahfi zai sami kariya daga Dajjal.”
(Muslim).

2. Haske a tsakanin sati biyu

Annabi ﷺ ya ce:

“Duk wanda ya karanta Suratul Kahfi a ranar Juma’a, zai sami haske tsakanin shi da Ka’aba.”
(al-Bayhaqi da al-Hakim s**a rawaito, s**a ce sahihi).

A wani riwayar:

“Duk wanda ya karanta Suratul Kahfi a ranar Juma’a, haske zai haska masa daga ƙasa zuwa sama, kuma zai haskaka masa tsakanin Juma’a biyu.”
(al-Hakim).

3. Kariyar daga fitintinu

Saboda surar ta ƙunshi labaran fitintinu da hanyoyin tsira daga gare su (fitinar addini, dukiya, ilimi, da mulki), wanda ya karanta ta da nazari Allah zai tsare shi daga irin waɗannan fitintinu.

4. Haske a kabari da ranar kiyama

An ce karatun Suratul Kahfi yana kawo haske a kabari, sannan kuma yana zama haske ga mai karatu a ranar kiyama.

Saboda haka, musulmi yana da kyau ya riƙa karanta Suratul Kahfi musamman a ranar Juma’a, ko da ya karanta cikakkiyar surar ko kuma ayoyi goma na farko
(ko na ƙarshe).

Kuyi sharing zuwa ga yan uwa su amfana

Abu Ja'afar Assunny ✍️

05/09/2025

🕌 GORON JUMA'A 🕌

(إِيَّاكَ نَعْبُدُ وَإِيَّاكَ نَسْتَعِينُ)
Kai kaɗai muke bauta wa, kuma Kai kaɗai muke neman taimako.
(Suratul Fātiha: 5)

📖 Ma’anar Aya:

إِيَّاكَ نَعْبُدُ – Wato Allah kaɗai ne muke bauta wa. Wannan yana nuna tawḥīd al-‘ibāda, cewa duk ibada sai ga Allah kaɗai ake yi.

وَإِيَّاكَ نَسْتَعِينُ – Wato Allah kaɗai ne muke neman taimako a wurinSa. Wannan yana nuna cewa duk wata nasara ko kariya daga Allah take.

✨ Darasi daga Aya:

Ibadar Musulmi ta tsarkaka domin Allah kaɗai 🕋

Babu wani aiki da zai yi nasara sai da taimakon Allah 🤲

Rayuwa ta Musulmi ta ginu a kan ibada da dogaro ga Allah 🌿

A yau mu ƙara yawaita:

Karatun Suratul Kahf

Yawaita salati ga Annabi ﷺ

Yin addu’a musamman bayan Asr har zuwa Magariba

Allah ya karɓi ibadunmu, ya taimake mu a duniya da lahira.

✨ Jumu‘at Mubarak! ✨

30/07/2025

Tufafin karshe, daga shi sai rayuwar karkashi, rayuwar Kabari, rayuwar bayan gari a karkashin kasa mai nauyin gaske.
Duk daren dadewa ni da kai sai an sanya mana wannan tufafin, daga lokacin mun tafi kenan babu mu babu labarin mu sai in mun bar alkhairi a bayan kasa kafin mu shiga karkashin ta.

Copied
-hadee isah Ibrahim

Address

Kano

Telephone

+2349162127245

Website

Alerts

Be the first to know and let us send you an email when Tunatarwa A Shari'ar Muslunci posts news and promotions. Your email address will not be used for any other purpose, and you can unsubscribe at any time.

Share