19/07/2020
Falalar Goman Farko Ta Zul-Hajji
An karbo Hadisi Daga ibn Abbas (R.A) ya ce
Annabi (SAW) ya ce:
Ranar daya ga watan zilhijja ita ce ranar da Allah
(swt) ya gafartawa Annabi Adam (A.S). Duk
wanda ya azimci wannan rana Allah(SWT) zai
gafarta masa kowane irin zunubi tsakaninsa da
shi.
(2) Ranar biyu ga Zulhijja ita ce ranar da Allah
(SWT) ya karbi Addu’ar Annabi Yunus (A.S) ya
fitar da shi daga cikin kifin da ya hadiye shi.
Wanda ya azimci wannan rana yana da lada
kwatankwacin wanda ya raya shekara da ibada .
(3) Ranar uku ga Zulhijja ita ce ranar da Allah
(SWT) ya karbi addu’ar Annabi Zakariyya (A.S)
ya ba shi haihuwa. Duk wanda ya azimci wannan
rana Allah (SWT) zai karbi adduo’insa.
(4) Ranar hudu ga Zulhijja ita ce ranar da aka
haifi
Annabi Isah (A.S). Duk wanda ya azimci wannan
rana Allah zai kare shi daga talauci da musibu.
(5) Ranar biyar ga Zulhijja ita ce ranar da aka
haifi
Annabi Musa (A.S). Duk Wanda ya azimci
wannan rana Allah (SWT) zai kare shi daga
munafunci ko azabar kabari.
(6) Ranar shida ga Zilhijja ita ce ranar da Allah
(SWT) ya yi budin alkhairi ga Annabi (SAW). Duk
wanda ya azimci wannan rana Allah zai dube shi
da rahama, kuma ba zai azabtar da shi ba.
(7) Ranar bakwai ga Zulhijja ita ce ranar da Allah
(SWT) zai sa a rufe kofofin wuta, ba za a bude su
ba har sai wadannan kwanaki goma sun wuce.
Duk wanda ya azimci wannan rana Allah zai rufe
masa kofofi talatin na tsanani a rayuwarsa a
buda masa kofofi talatin na sauki.
(8) Ranar takwas ga Zilhijja ita ce ranar da ake
cewa, ranar tarayya. Duk wanda ya azimci
wannan ranar, babu wanda ya san adadinsa sai
Allah.
(9) Ranar tara ga watan Zulhijja ita ce ranar
hawan Arfa. Allah yana gafartawa duk Alhazan da
ke wurin Arfa. Wanda kuma ba ya wurin aikin
Hajji, idan ya azimci wannan ranar, Allah yana
gafarta masa zunibinsa na shekarar da ta
gabata,
da kuma shekarar da ke tafe.
(10). Ranar goma ga Zulhijja ita ce ranar layya.
Duk wanda Allah ya horewa. From Sen Aliyu Suleman Ibrahim