30/04/2024
Abun Ayaba Jami'in Ɗan Sanda Ya Ƙi Karɓar Cin Hancin Naira Miliyan 150 a Jihar Adamawa
Wani jami'in ɗan sanda mai suna Ibrahim Ezekiel Sini, ya ƙi ƙarbar cin hanci na miliyoyin Naira a jihar Adamawa.
Kuɗin da yawan su ya kai Naira miliyan ɗari da hamsin (N150,000,000.00), an yi masa tayin su ne domin ya saki wani wanda ake tuhuma da zambar kuɗi Dalar Amurka kimanin Dala milliyan shida ($6m).
Yanzu haka dai jami'in ɗan sanda yana shan yabo ta ko'ina musamman daga al'ummar ƙaramar hukumar Michika a jihar Adamawa inda nan ne lamarin ya faru kuma har an karrama shi da lambar yabo.
Attached to Central mouq